Saturday, 31 December 2016

Wani dan bindiga ya kashe mutum 39 a Turkiyya

Wani mutum dauke da bindiga ya kashe mutum
39 sannan ya jikkata 40, a wani hari da ya kai
gidan rawa.
Harin wanda aka kai a birnin Istanbul na
Turkiyyar, ya janyo mutane da dama sun kuma
fada cikin kogi sakamakon gudun ceto rai.
Kididdiga dai ta nuna akwai mutum fiye da 700 a
gidan rawar lokacin da abin ya faku.
Kafofin watsa labaran kasar sun ce mutumin ya
yi shigar burtu ne, har ya samu ya shiga gidan
rawar.
Daga nan kuma sai ya bude wuta a inda nan
take ya kashe mutanen.
Rahotannin dai sun tabbatar da cewa dan sanda
daya na daga cikin mamatan.
Daman dai akwai 'yan sandan ko-ta-kwana fiye
da dubu 16 a birnin na Istanbul saboda yawaitar
hare-haren ta'addanci.
Ko a makonni biyun da suka gabata ma sai da
aka harbe jakadan kasar Russia har lahira.
Sau shida ne dai hare-haren da ke haddasa
mutuwa da jikkatar mutane suka faru a 2016 a
kasar musamman a biranen Ankara da Istanbul.
Kuma fiye da mutane 200 sun mutu a hare-haren
guda shida.

Ni ma zan iya amfani da karfi kan ECOWAS — Jammeh

Shugaban Gambia mai barin gado, Yahaya
Jammeh, ya ce, idan tura ta kai bango zai iya
yakar Kungiyar Habaka Tattalin arzikin Afirka ta
Yamma, ECOWAS ko kuma CEDEAO.
A wani sakon taya murnar sabuwar shekara ga
'yan kasar, da aka yada a kafar sada zumunta ta
Youtube, Jammeh, ya ce, kungiyar na wuce gona
da iri a Gambia.
Ya ce ECOWAS na nuna banbanci tsakaninsa da
Adama Barrow.
Saboda haka ne ya nemi kungiyar da ta san inda
dare ya yi mata domin a cewarsa bata da
hurumin yin katsalanda a kasar.
Yahya Jammeh dai ya ce shi ne mutumin da ya
lashe zaben kasar na farkon watan Disambar
2016, bayan da da fari ya amince da shan kaye.
Kungiyar ECOWAS dai a taron da ta yi a Abuja,
babban birnin Najeriya, ta ce, za ta iya amfani
da karfi wajen tunbuke Yahya Jammeh.

An tsaurara matakai yayin da shekarar 2017 ke kamawa

An tsaurara matakan tsaro a manyan biranen
duniya yayin da ake shirin shiga sabuwar
shekara ta 2017.
A wasu biranen kasashen yamma, da suka hada
da London, da Brussels da Berlin, an girke karin
dubban 'yan sanda gabanin bukukuwan shiga
sabuwar shekarar.
An sanya shingaye na kankare a wuraren taruwar
jama'a a tsakiyar birnin Paris, da Madrid da New
York don kare aukuwar hare-hare da manyan
motoci, kwatan-kwacin wadanda aka kai a baya a
biranen Berlin da Nice.
An hana jama'a yin shagulgulan sabuwar
shekarar a Dhaka, babban birnin Bangladesh,
wanda ya yi fama da hare-haren 'yan bindiga
masu alakanta kansu da Musulunci.

YADDA AKE WANKAN JANABA DANA BIKI DA WANKAN HAILA DA SAURANSU

YADDA AKE WANKAN JANABA, HAILA, BIKI DA
DAI SAURAN SU.
Daga Marigayi Sheikh Jafar Mahmud Adam Kano.
Wankan Janaba yana da siffa guda biyu: Akwai
'siffatul ijza' (ta wadatar), kuma wacce ake kira
'siffatu kamal' (ta kamala).
Wankan Janaba a siffar sa ta kamala shi ne:
Idan kazo zaka yi ko za kiyi wanka ga ruwa a
gabanka. Farkon abin da zaka fara yi shi ne:
zaka karkato bakin mazubin ruwanka, ka wanke
hannunka sau uku, sannan sai ka tsoma hannu a
cikin ruwan sai ka debo ka wanke gaban ka ، a
dai-dai lokacin da zaka wanke gaban ka a lokacin
zaka kulla niyya ta wankan janaba (Ko waninsa)
wanda yake wajibi ne, idan ka wanke gabanka
ma'ana kayi tsarki kenan ، to daga nan kuma sai
kayi alwala irin yanda kake alwala ta sallah, abin
da duk kake a alwala ta sallah zakayi sai abu
daya shi ne wanke kafafu to wannan zaka kyale
shi ba zaka yi shiba, to daga nan sai ka tsoma
hannunka guda biyu a cikin ruwan ba tare da ka
debo ruwa ba sai ka murmurza kanka saboda
kowane gashi da ya bude a lokacin da maniyyi
yake kokarin fita daga jikinka ya koma yanda
yake, don gashin dan Adam yakan bude
musammam gashin sa na ka, idan ka zuba ruwa
a haka na iya haifar maka da ciwon kai ko wani
abu daban, bayan haka sai ka debi ruwa a cikin
tafin hannun ka daya sai ka zuba a kanka ka
tabbatar ya game ko'ina a kanka, ka sake
kanfata na biyu ka tabbatar ya game ko'ina a
kanka, haka na uku ka tabbatar ya game ko'ina a
kanka.
To idan kayi wannan sai ka debi ruwa ka game
dukkanin jikin ka da shi kana mai farawa da
bangaren jikin ka na dama kafin na hagu, sannan
na hagu ka tabbatar ruwa ya taba ko'ina. To idan
kayi wannan ne ka kammala, abu na karshe shi
ne sai ka wanke kafar ka ta dama sannan
kafarka ta hagu shine cikon alwalar da ka riga ka
faro. Wannan ita ce siffa ta kamala a wankan
janaba.
In wankan janaba ne haka zakayi, in na haila ne
haka za'ayi inma wanka ne na biki haka mace
zata yi, idan wankan jumu'a ne ma haka za'ayi,
wankan idi ma haka zaka yi, banbanci kawai shi
ne NIYYA.
Idan mutum zai yi siffa ta 'Al ijza' wadda ta
wadatar ba sai kayi alawa acikin ta ba, kana
zuwa kayi niyyar yin wanka din kawai sai ka
dauki ruwan ka watsa a jikin ka ya game ko'ina,
inma wani kududdufi ne ko rami ko swimming
pool sai kayi tsalle ka fada aciki, dama ka kulla
niyyar ka kafin ka shiga, daga ka fito abin da
zakayi shi ne abubuwa guda biyu, kurkurar baki
da kuma shaka ruwa a hanci da facewa.
Shike nan, kuma ya halatta kayi sallah da
wannan wankan, Hadisi cikin Sahihu Muslim ya
nuna haka.
Sai dai wanda ya yi wanka na farko ya fika
kamala saboda ya bi dukkan sharuddan, ya fika
cikar kamala, ya fika lada.
Kasancewar ba'ayi alwala ba ciki, wannan
ka'idace ta malamai cewa karamin kari
(HADATHUL ASGAR) idan sun hadu da babban
kari (HADATHUL AKBAR) to da ka kawar da
babban kari, karamin ma ya tafi. Amma ba lallai
bane idan ka kawar da karamin ace babban ma
ya tafi.
Bissalam

Buhari ya musanta korar Ibrahim Magu daga aiki

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya
musanta rahotannin da wasu kakafen watsa
labarai na kasar suka bayar cewa ya kori
shugaban hukumar da ke yaki da masu yi wa
tattalin arzikin kasar ta'annati, EFCC, Ibrahim
Magu daga aiki.
Wata sanarwa da kakakin shugaban kasar Malam
Garba Shehu ya fitar ranar Asabar ta ce masu
watsa irin wadannan rahotanni suna yin shaci-
fadi ne kawai.
A cewarsa, "Mun karanta rahotannin cewa an
sallami shugaban EFCC, Ibrahim Magu daga aiki.
Babu wani rohoto da babban mai shari'a na kasa,
wato Antoni Janar ya mika wa fadar shugaban
kasa a kan wannan batu. Don haka rahotannin da
ke cewa an kore shi daga aiki shaci-fadi ne
kawai".
Ibrahim Magu dai ya shiga bakin 'yan jarida sosai
tun bayan da majalisar dattawan kasar taki
amincewa ta tabbatar da shi a matsayin
shugaban EFCC, tana mai cewa ta dauki matakin
ne sakamakon wani rahoton sirri da hukumar
tsaro ta farin-kaya, DSS ta mika mata a kansa
wanda ke nuna cewa ya aikata ba daidai ba.
Sai dai masu fashin-bakin siyasa na ganin an ki
tabbatar da Mr Magu a kan mukaminsa ne
saboda takun-sakar da ake yi tsakaninsa da
shugaban DSS ba wai domin ya aikata wani laifi
ba.
A kwanakin baya ne kakakin shugaban kasar ya
ce Shugaba Buhari ya bayar da umarni ga
ministan shari'ar kasar ya yi bincike kan wasu
manyan jami'an gwamnatinsa bisa zarginsu da
aikata ba daidai ba.
Kodayake bai ambaci mutanen da za a yi bincike
a kan nasu ba, amma rahotanni na cewa Ibrahim
Magu da Sakataren gwamnatin tarayya, Babachir
Lawal su ne mutanen da za a yi bincike a kansu.
Shi dai Ibrahim Magu ta taka sawun manyan
mutane da dama a yakin da yake yi da cin hanci
da rashawa, cikin su har da Kanar Sambo
Dasuki, tsohon mai bai wa tsohon shugaban
kasar shawara a kan sha'anin tsaro da kuma
tsofaffin manyan jami'an rundunar sojan kasar,
wadanda ake zargi da sace kudin da aka ware
domin yaki da kungiyar Boko Haram.

YOU MAY ALSO LIKE: NURA M INUWA FT ALI SHOW NEW ALBUM RUMAH

Make up designer

Nigeria: Ƙkaunar Buhari na neman hada faɗa

A Najeriya, yayin da aka ga kamun ludayin
gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari, an fara
samun saɓanin ra'ayi tsakanin magoya bayansa
sakamakon matakin da wasu daga ciki ke ɗauka
na sukar wasu manufofin gwamnatinsa.
`Yan ga-ni-kashe-nin shugaban kasar dai na cewa
shugaba Buhari ba ya laifi, don haka bai kamata
a kushe masa ba, inda sukan maida raddi da
kakkausar kalamai idan ana muhawara da su kai-
tsaye ko ta shafukan sada-zumunta na zamani,
lamarin da ke rage tagomashin shugaban kasar a
zukatan masu sassaucin ra`ayi.
Duk da cewa duka ƙaunar mutum guda ce ta
haɗa su, masu sassaucin ra`ayi na ganin cewa
ba daidai ba ne su yi shiru a duk inda suka ga
shugaban kasar ya yi kuskure, saboda a ra`ayin
irin waɗannan mutane, mutum tara yake bai cika
goma ba, don haka kamar sauran jama'a,
shugaban kasar bai fi ƙarfin yin kuskure ba, kuma
yi masa gyara ko tsokaci wata siga ce ta ƙauna.
Sai dai ɓangaren shugaban kasar ya ce
demokradiyya ta gaji yabo da suka, don haka
babu dalilin fada da juna.
Masana dai na ganin cewa magoya bayan
shugaba Buhari na bukatar sake-lale a
muhawararsu, saboda masu sassaucin ra`ayi na
cewa azalzalar da `yan ga-ni-kashe-ni ke musu ta
sa ƙaunar da suke yi wa shugaban kasar ta fara
gushewa a hankali.

Friday, 30 December 2016

Babu shinkafar roba a Nigeria - NAFDAC

Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna
ta Najeriya (NAFDAC) ta ce sakamakon gwajin
da aka yiwa shinkafar da jami'an hukumar
kwastam na kasar suka kwace ya nuna cewa
shinkafar gurbatacciya ce ba ta roba ba.
Wani babban jami'i a hukumar ya ce shinkafar
dai na dauke da kwayar cutar bakteriya ne wadda
ta wuce adadin da aka amince da ita.
Jami'an hukumar ta kwastam sun hakikance
cewa shinkafar da suka kwace a Lagos a makon
jiya ta roba ce, lamarin da ya haifar da cece-
kuce har ministan lafiya na kasar ya shiga
tsakani yana mai cewa ba bu wata shaida da ta
tabbatar da hakan.
Gwajin da aka yiwa shinkafar dai ya tabbatar da
cewa amfani da ita zai iya haifar da illa ga
al'umma saboda kwayar cutar bakteriyar da ke
cikin shinkafar ta wuce kima.
Hukumar kwastam ta ce ta kwace shinkafar ne
bisa bayanan da ta samu cewa za a shigo da
shinkafar roba mai yawa daga Asiya zuwa Afrika.
Duk da cewa sakamakon gwajin shinkafar ya
tabbatar da cewa gurbatacciya ce, har yanzu
wasu bayanai sun nuna cewa akwai tan-tan na
lalatacciyar shinkafa da aka ajiye a rumbunan
tara abinci da ke kasashe makwabta.
Shinkafa dai itace abinci na farko da 'yan
Najeriya suka fi amfani da ita, kuma itace akafi
bayarwa kyauta idan wani sha'ani ya tasowa
mutum.

Make up designer

NURA M INUWA IN STUDIO SINGING NEW WEDDING SONG

NURA M INUWA IN STUDIO SINGING NEW ALBUM DAN MAGORI

KOREDE BELLO SINGING WHY U GONE DO LIKE THAT

Wednesday, 28 December 2016

Ina Nan Daram A cikin Addinin Musulunci – Inji Rahama Sadau

Shahararriyar yar wasan kwaikwayon nan ta kannywood, Rahama Sadau ta maida martani dangane da wani audio na jita-jita da aka rinka yadawa a kafar sadarwa ta WhatsApp kan cewar wai zata bar addinin Musulunci sakamakon tayi da aka yi mata da wasu miliyoyin dalolili, da kuma samun masayin matsayin shiga masana'antar wasan kwaikwayo ta Hollywood.
Ta bayyana cewa wannan zance ne da bashi da tushe ko makama wanda kuma an kirkire shi ne don a bata mata suna, inda ta nuna damuwa matuka sannan kuma ta bukaci jama'a da suyi watsi da wannan recording na audio da ake yadawa. Ta kara da cewar sana'arta baza shafi addininta ba ballantana ma har ace zata sayar da imaninta wa wasu yan dalolili.

Idan zaku iya tunawa, a can bayane jarumar ta fito wani faifan Bidiyon waka tare da mawakin hiphop Classiq wanda hakan ya jawo kakkausar suka a gareta inda daga bisani hakan ya janyo
MOPPAN Ta kori Jarumar daga kannywood wanda sanadin hakan ne ta samu gayyata zuwa masana'antar fina-finai ta Hollywood dake kasar Amurka.
"Abin ya kona min rai matuka, musamman ma ta yadda har wasu manyan malamai suka yarda da wannan jita-jitar da aka rinka yadawa kuma suka yi amfani da ita wajen suka ta ba tare da sunyi bincike don tabbatar da sahihancin labarin ba, wanda hakan ya harzuka yan uwa da abokan arziki. Abisa wannan dalilin ne naga ya zama wajibi na fito in yiwa jama'a bayani. "
Ni Rahama Sadau inaso in shaidawa al'umma gami da jaddada musu cewar wannan zancen da ake yadawa akai karya ce mara tushe da aka kirkiro don a bata mun suna, saboda haka ina kira ga masoya na da su yi watsi da wannan jita-jitar. "
Ta kara da cewar" in baku manta ba, Akon wanda yake musulmi ne kuma dan asalin kasar Senegal ya fuskancin irin wannan kalubalen daga kafafen yada labarai na can kasar ta su. "
Tura wa abokanenka dake Facebook, Twitter, WhatsApp da sauransu.

Baturen Da Aka Kama A Sambisa Dan Faransa ne

A ranar Alhamis 22 ga watan Disamban nan data gabata ne rundunar sojin Nigeria ta samu nasarar kakkabe yan ta'adda na bokoharam daga dajin Sambisa dake jahar borno, inda yan ta'addan da yawa suka rasa rayukansu a yayin da kuma aka sami nasarar cafke wasu da ransu.
Idan baku manta ba munkawo muku rahoton cewa Sojoji Sun Kama Wani Farar Fata A Dajin Sambisa wanda ba'a bayyana ko dan wace kasa bane a lokacin sakamakon bincike da ake gudanarwa akan shi.
Jaridar Dailytrust ta Yau laraba ta ruwaito cewar wannan baturen da sojoji suka kama yayin dauki ba dadi a dajin Sambisa dan kasar Faransa ne wanda ya kasance kwararre a bangaren sarrafa gami da gyara manya-manyan makamai da yan bokoharam ke amfani da su, a yadda jaridar ta samu labari daga majiya mai karfi.
Gwamnati taki bayyana bayanan baturen da aka kama ne saboda halin zamantake wa gami da kuma karin bincike da ake yi don kara tatso bayanai daga gurin shi wanda aka kama din.
"an kama shi ne a kewayen Bama inda yayi alkawarin bayar da bayanai masu mahimmanci ga jami'an tsaro. An gano cewa dan France ne, amma hukumomin tsaro basu so a bayyana hakan saboda hali diplomasiyya da kuma gudun mayar da hannun agogo baya bisa nasarar da aka samu.
Sai dai a yayin da aka tuntubi ofishin jakadancin kasar Faransa dake dake Nigeria ta sakon email don jin ta bakinsu dangane da lamarin basu ce komai ba.
Yan Nigeria dai sun kasa kunne don jin abinda hukumomin tsaron kasar zasu ce dangane dashi wannan farar fata da aka kama..
Tura zuwa abokanenka dake Facebook, Twitter, WhatsApp da sauransu.

Tuesday, 27 December 2016

'Za mu mayar da dajin Sambisa wurin atisayenmu'

Hukumomin soji a Nigeria sun ce za su mayar da dajin Sambisa - inda ya kasance sansanin mayakan Boko Haram tun shekara ta 2013 - wurin atisaye.
A makon jiya ne dai shugaban kasar, Muhammadu Buhari, ya tabbatar da cewa sojojin sun yi nasarar kwace dajin daga hannun mayakan.
Mai magana da yawun rundunar sojin kasa Birgediya-Janar Sani Usman Kukasheka ya shaida wa BBC cewa za a yi hakan ne domin tabbatar da cewa ''wasu miyagun mutane ba su fake a wannan dajin ba.''
Janar Kukasheka ya ce kuma nan gaba kadan za su yi wa 'yan kasar bayanin abubuwan suka tarar a dajin bayan fattatakar mayakan Boko Haram daga sansanoninsu.

Apple zai fara kera mota mara matuki

Kamfanin Apple ya ce yana shirin soma kera motoci marasa matuka.
A wata wasika da ya aike wa hukumar da ke sanya ido kan sufuri ta Amurka, Apple ya ce yana "matuka murna kan yadda fannin fasaha ke sauyawa ciki har da fannin sufuri".
Ya kara da cewa al'uma za ta mori sauye-sauyen da ake samu a motocin da ake kerawa marasa matuka.
An dade ana rade-radin cewa Apple zai soma kera motoci marasa matuka, amma sai yanzu kamfanin ya tabbatar da batun.

How To Block Pop-up Ads On Your Android Phone

Evening, this is not the first time i am posting such a write up of which if adhered strictly will surely help you get rid of some annoying intrusive pop ads incoperated in some applications installed on your android phones.
Many application developers are providing us with free services in their softwares at which they in return serve some adverts so as to generate income with which they'll continue to stay in the business, as the user, you reap the benefit of using the product for free.
In their quest to gather huge amount of money within a space of a very short period of time, some apps developers tend to abuse the chance they’ve gotten as they place too much of the adverts in
such a way that the ads prevent the user from enjoying the benefits that app was created for.Therefore a need to block some of these annoying adverts arises so that you inhale a fresh air as you use such of these apps. So grab your cup of Coffee, sip small and keep following Amanagurus
Disclaimer: Blockage of ads using any of these apps should be done at holder's risk. We cannot be held responsible for any effects on your device resulting from the methods shared.
We'll be making use of these two third party apps which are quite good in ads blocking, but prior to that, there might arise a requirement for a root access ;
- Lucky Patcher apk ( download it Here )
Adblock Plus is an open source project which has the capacity to allow non-intrusive ads. This app works on both rooted and non-rooted devices, but our emphasis will be on rooted phones. Installing an ad-blocker app requires your device to allow applications from unknown sources.
To allow installation of apps from unknown source you:
- Go to Settings> Security
-Navigate to the Unknown sources
option.
- If unchecked, tap the checkbox, and then tap OK on the confirmation popup.
Your Android device is ready to install any sideloaded app, including this ad-blocker you've downloaded...
Ensure that your device is rooted prior to the installation of this great application. I recommend Kingroot apk for the rooting process.
Having rooted your phone and enabled installs from unknown source, you just go ahead and install the app on your device, after installing,
open the app (Adblock Plus) It will request for super user permissions. Allow super user permissions to Adblock Plus and you are done.
The second app we'll be making use of is the Lucky patcher apk
. Lucky patcher is a great Android app which lets you remove adverts from Android apps and games , modify permissions of different apps, bypass license verification of premium apps, backup downloaded apps and games and many more other tasks.
Just download and install it on your device from this Link.....
I am pretty sure that you could be able to at this juncture get rid of some annoying intrusive ads on your android phone. Your friend might be facing a similar issue hence a need to share it to your fb timeline, WhatsApp groups, twitter and soon..

Boko Haram: Jam'iyyar PDP ta yaba wa Shugaba Buhari

Babbar jam'iyyar hamayya ta Nigeria PDP ta yaba wa shugaban kasar Muhammadu Buhari bisa nasarar kakkabe 'yan Boko-Haram daga dajin Sambisa.
PDP ta ce ta jinjina wa Buhari bisa tsayuwar-dakan da ya yi a yakin da ake yi da 'yan Boko Haram.
Haka kuma jam'iyyar ta nuna farin ciki kan abin da ta ce ci-gaba da Buhari ya yi a kan kokarin da gwamnatin Goodluck Jonathan na PDP ta yi a yakin da ta'addanci.
Wata sanarwar da sakataren watsa labaran jam'iyyar Price Dayo Adoyeye ya fitar ta ce nasarar da aka samu a yakin da ake yi da Boko Haram ta samo tushe ne daga irin kokarin da gwamnatin baya ta yi, musamman 'yan makwanni, gabanin gudanar da zaben shuugaban kasa a shekarar 2015.
Sanarwar ta PDP ta kuma jinjina wa sojojin Nigeria bisa jajircewa a yukurin raba kasar da masu tada kayar baya.
To sai dai PDP ta ce kwace dajin Sambisa ba ya nufin cewa an kammala yaki da ta'addanci, ta yi kira hukumomin Nigeria su matsa-kaimi wajen kakkabe 'yan ta'adda daga dazukan kasar da dama da suka zama wata mafaka ga 'yan ta'adda.
Ba kasafai dai PDP ke yabawa Buhari ba, kuma a lokuta da dama tana caccakarsa kan koma baya a bangaren tattalin arziki.

Monday, 26 December 2016

Amurka ce kanwa-uwar gami — Netanyahu

Firai ministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya zargi Amurka da kitsa kudirin da Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya fitar na haramta mata yin gine-gine a yankin Falasdinawa.
Mista Netanyahu ya yi wannan zargin ne lokacin da ya gayyaci jakadan Amurka a kasar domin fayyace dalilin da ya sa Amurkar ta juya mata baya a wannan lokaci.
A ranar Juma'a ne dai Kwamitin Sulhun na MDD ya kada kuri'ar amincewa da kudirin da ya haramta wa Isra'ila cigaba da gine-gine a Gabar kogin Syria da Gabashin birnin Jerusalam.
Kuma Amuka ta kame bakinta daga hana kada kuri'ar kamar yadda ta saba a baya, a inda ta sha yin karfa-karfa.
Rasha da China da Burtaniya da Faransa sun goyi bayan wannan sabon kudiri.
Sharhi, Usman Minjibir
Da man dai Netanyahu ya zargi gwamnatin Barack Obama da nuna halin ko-in-kula da yanayin tsaron Isra'ila.
Hakan ne ya sa mista Netanyahu yin alwashin tafiya tare da zababben shugaban Amurkar, Donald Trump.
Mista Trump ya sha fadin cewa zai warware duk wasu matakan da aka dauka a kan Isra'ila da zarar ya hau mulki.
Donald Trump dai yana kokarin dawo da hannun agogo baya musamman ga wasu ayyuka da hukunce-hukuncen da gwamnatin Obama ta dauka.
Isra'ila na aikata haramci —Ban Ki-Moon
Ana yunkurin diplomasiya kan rikicin Isra'ila da Palasdinu
Wannan dai ba shi ne karon farko da ake yi wa irin ayyukan Isra'ila kallon haramtattu ba a yankin Falasdinu.
Ko a baya-bayan nan sai da Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya mai barin gado, Ban-Ki Moon, ya ce, Isra'ila na aikata haramci.

Ba za mu yi rijista ba tun da ba kungiya ba ce — Shi'a

Harka islamiyya ko kuma Islamic Movement of Nigeria ta mabiya mazhabar Shi'a, ta ce ba za ta yi rijista ba, domin kira take yi, ba kungiya ba ce.
Wani jami'in tafiyar, Barista Haruna Magashi ne ya bayyana hakan a wani taron sasanta rikicin 'yan Shi'ah da 'yan sanda, a jihar Kano.
Tun da farko, mataimakin kwamishinan 'yan sanda, Toluse O. Emmanuel ya nanata cewa matukar mutum ko kungiya suka nemi izinin yin 'halartaccen' taro, ba shakka 'yan sanda za su ba su dama.
Barista Magashi ya koka a kan yadda mutane ke 'shayin' kusantarsu don jin abin da tafiyarsu ta kunsa daga bakinsu.
Wani mai gabatar da mukala a taron, Prince Ajayi Memaiyetan ya soki lamirin yadda 'yan sanda ke amfani da bindiga don tarwatsa jerin gwanon 'yan Shi'a.
Sai dai kuma wasu masu magana da dama a wurin taron, sun ce ba dai-dai ba ne yadda harka islamiyya ke gudanar da taro, ba tare da neman izinin hukuma ba.
Wannan dai wani matakin farko ne na tattaunawa kan rikicin 'yan Shi'a da jami'an tsaro kuma ya samu wakilcin mabiya addinai daban-daban.
Sharhi, Usman Minjibir
Tun dai watan Disambar 2015, lokacin da gwamnatin Najeriya ta kama shugaban Islamic Movement of Nigeria, Sheikh Ibahim El-zakzaky, mabiya malamin ke ta faman yin jerin gwano domin ganin an sake shi.
To sai dai jami'an tsaro musamman 'yan sanda na ganin jerin gwanon ya saba dokar kasa saboda rashin neman izni.
'Yan uwa musulmi dai na cewa koda sun nemi izni a wurin 'yan sanda ba za su ba su ba.
Babban al'amarin da ya faru tsakanin 'yan sanda da 'yan Shi'a, a baya-bayan nan, shi ne, lokacin da 'yan sanda suka tarwatsa wani tattaki da 'yan Shi'ar suka so yi daga birnin Kano zuwa Zaria.
Mutane da dama dai sun rasa ransu sannan wasu da dama sun jikkata.

Wednesday, 21 December 2016

Nigeria: Kwastam ta kama shinakafar da aka yi da roba

Hukumar hana fasa kwauri ta Nigeria kwastam ta ce ta kama buhu 102 na wata sinkafar da aka yi da roba wacce aka shigar da ita kasar ta barauniyar hanya.
Wani babban jami'in hukumar ya ce wani dan kasuwa ne ya shigar da shinkafar domin sayarwa a lokacin bukuwan kirsimeti.
Jami'in mai kula da shiyya ta daya ta hukumar hana fasa kwauri da ke Ikeja Haruna Mamudu, yace binciken farko ya nuna cewa shinakafar ta roba tana cabewa idan an tafasa ta, sanan ya ce Allah ne kadai ya san irin illar da za ta yi wa duk wanda ya ci.
Sai dai Harun Mamudu bai bayyana yadda aka yi shinkafar ba, to sai dai ya ce sunanta "best Tomato Rice".
Ya kara da cewa ana gudanar da bincike don gano irin wannan shinkafa ta roba da ake sayarwa a kasuwa.
Wani jami'in hukumar ya shedawa BBC cewa an kama mutum daya dan Nigeria, sai dai har yanzu suna bincike don sanin daga inda aka shigar da shinkafar kasar.

Tuesday, 20 December 2016

Zamu magance matsalar tsaro a Kudancin Kaduna-El Rufai

A Nigeria, gwamnatin jahar Kaduna ta sha alwashin magance matsalolin tsaron da ake fama da su a kudancin jahar.
Gwamnan jihar Malam Nasir El-Rufai shi ne ya bayyana haka yayin wata ziyara da ya kai tare da wasu jami'an gwamnatin jahar zuwa garin Kafanchan karamar hukumar Jama'a inda aka tafka rikici a ranar litinin din da ta gabata.
Gwamnatin jahar ta zargi wasu 'yan siyasar yankin da ingiza zanga-zangar da ta haddasa rikicin da ya haifar da asarar rayuka da dukiyoyi.
Wasu 'yan yankin kudancin jihar dai sun gudanar da karin zanga-zanga a yayin ziyarar da gwamnan ya kai duk da dokar hana fitar da aka sanya a garin na Kafanchan.

Nigeria: Mata sun yi zanga-zanga tsirara, suka fasa motocin El-rufa'i

Wasu fusatattun mata sun yi zanga-zanga tsirara a yankin Kudancin Kaduna, kwana daya bayan wani rikici da aka yi a Kafanchan.
Mutane da dama aka kashe sakamakon rikicin da ya barke lokacin da matasan yankin suka yi wata zanga-zanga a ranar Litinin.
Matan sun yi zanga-zangar ne yayin da tawagar gwamnan jihar Malam Nasir El-rufa'i ta kai ziyara yankin, don ganin irin ta'adin da aka yi.
Fisatattun sun kuma farfasa motocin tawagar gwamnan sakamakon jefe-jefe da suka ringa yi da duwatsu.
Masu zanga-zangar dai sun fito ne duk kuwa da dokar hana fita ta tsawon sa'o'i 24 da aka ayyana, inda suka ce sun gaji da kashe-kashen mutane da ake yi a yankin.
Tun da farko dai, gwamnan jihar ta Kaduna ya yi wa matan jawabi, sannan ya kuma amsa tambayoyinsu.
Wakilin BBC da ke cikin tawagar ya ce zanga-zanagr matan tsirara ta kunyata duka mutanen da suka halarci wajen.
Gwamna El-rufa'i ya shaida wa matan an kara daukar matakan tsaro domin kawo karshen rikici a yankin.
Wakilinmu ya ce an yi ta'adi sosai yayin zanga-zangar da aka yi ranar Litinin wacce ta rikide zuwa kone-konen wurare, ciki har da masallatai da kuma coci-coci.

Magajin gari

Chioma Obiadi: Kalli matar da ta fi 'kowacce kyau' a Nigeria

An zabi Chioma Obiadi a matsayin sarauniyar kyau ta Najeriya ta bana bayan gasar da aka gudanar karo na 40 a birnin Lagos.
Mis Obiadi, wacce 'yar asalin jihar Anambra ce, ta doke Mis Blessing Obila daga Ebonyi, yayin da Mis Shade daga Kwara ta zo ta uku.
Kamfanin dillancin labarai (NAN), ya ruwaito cewa an fara gasar ne tun shekarar 1957.
Mata 38 ne suka shiga gasar bana daga jihohin kasar da kuma birnin tarayya Abuja, wacce aka gudanar a otel din Eko Hotel and Suite da ke Lagos.
An fara tankade 'yan takara daga 38 zuwa 10 kafin su koma uku.
Kamfanin jaridar Daily Times ne ke shirya gasar tare da hadin gwiwar wasu kamfanoni masu zaman kansu.
Da ta ke magana da NAN, wacce ta zo ta biyu Obila, wacce ta yi karatu a jami'ar jihar Akwa Ibom, ta bayyana jin dadinta game da nasarar da ta samu.
Rahotanni sun ce taron ya yi armashi inda ya samu halartar masu kade-kade da raye-raye daga sassan kasar da dama, cikin har da matar da ta fara lashe kyautar Misis Grace Oyelude.

Monday, 19 December 2016

Nigeria: Buhari ya sa a binciki 'Babachir Lawal da Ibrahim Magu'

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya sa a binciki Sakataren gwamnatin kasar Babachir Lawal da wasu manyan jami'an gwamnati da ake zargi da aikata cin hanci da rashawa.
Mista Lawal da shugaban riko na Hukumar yaki da cin hanci ta EFCC Ibrahim Magu, na daga cikin wadanda rahotanni suka ce za a bincika.
Wata sanarwa da fadar shugaban ta fitar, wacce ba ta ambaci sunan kowa ba, ta ce babu sani ba sabo a yaki da cin hanci da rashawar da gwamnati ke yi, kuma duk wanda aka samu da laifi ba zai tsira ba.
A makon da ya gabata ne wani rahoton majalisar dattawan kasar ya zargi Mista Lawal da bayar da kwangilar miliyoyin naira ga wani kamfaninsa.
Har ila yau an zargi kamfanin da gazawa wurin gudanar da aikin da aka bashi a wani bangare na shirin kula da 'yan gudun hijirar da Boko Haram ta fatattaka daga gidajensu.
Sai dai babban jami'in, wanda na da kusanci sosai da Shugaba Buhari, ya musanta zargin aikata ba daidai ba.
Ba ya ga Babachir, wasu rahotanni na nuna cewa har da Shugaban Hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta kasar EFCC, Ibrahim Magu, za a bincika.
A makon da ya gabata ne 'yan majalisar dattawa suka ki amincewa su tabbatar da shi a kan kujerarsa saboda zarginsa da sabawa ka'idojin aiki.
An zargi Mista Magu da karbar gida daga hannun wani tsohon jami'in rundunar sojin sama ta kasar, batun da ya musanta.
Mai magana da yawun shugaban Garba Shehu, ya ce an umarci Ministan Shari'ar Kasar, Abubakar Malami, da ya gudanar da bincike domin gano gaskiyar abin da ke gudana.
Tun bayan hawansa kan mulki, Shugaba Buhari ya kama manyan jami'an tsohuwar gwamnati wadanda tuni aka fara yi wa wasunsu shari'a kan zargi aikata laifukan da suka shafi cin hanci da rashawa.
Masu sukar gwamnatin ta APC dai na cewa ta mayar da jami'anta shafaffu da mai, yayin da kawai take tuhumar 'yan adawa.

Sunday, 18 December 2016

Real Madrid ta lashe kofin duniya na zakarun nahiyoyi

Real Madrid ta ci kofin duniya na zakarun nahiyoyi, bayan da ta doke Kashima Antlers da ci 4-2 a fafatawar da suka yi a ranar Lahadi.
Real Madrid ta ci kwallon farko ta hannun Kareem Benzema a minti na tara da fara tamaula, sannan Cristiano Ronaldo ya kara ta biyu a bugun fenariti a minti na 60 ana murza-leda.
Ita kuwa Kashima Antlers ta fara cin kwallo ne ta hannun Gaku Shibasaki daf da za a je hutun rabin lokaci, kuma bayan da aka dawo ne daga hutun ya kara cin ta biyu.
Haka aka tashi wasa 2-2 daga nan ne ka yi karin lokaci na minti 30, wasan farko minti 15 ya sake fafatawa karo na biyu minti 15.
Nan ne fa Real Madrid ta samu damar kara cin kwallaye biyu ta hannun Cristiano Ronaldo, wanda hakan ya sa ta lashe kofin duniya na zakarun nahiyoyi.
Wannan ne karo na biyu da Madrid ta ci kofin bayan wanda ta dauka a 2014

Yanda Zaka Rage Wa Video Nauyi Ta Amfani Da Wayar Android

Jama'a barkanku da warhaka, Amanagurus ne ke muku lale marhabun da zuwa shafin mu mai albarka na arewamobile wanda ke kawo muku bayanai akan matsaloli da suka shafi wayoyin hannu da kuma bayanai kan manyan na'urori da sauran makamantan hakan.
A yau in sha Allahu zanyi bayani kan yadda zaku iya rage nauyin video ta hanyar amfani da wasu manhajoji na wayar hannu ta android wacce take mazaunin wayar da aka fi amfani da a wannan lokaci da muke ciki.
A bayyane yake cewar kowa na son ganin hoton video mai kyau (High defination) yayin da yake kallo musamman kallon fina-fina na cikin gida har ma zuwa na waje don jin dadin abinda mutum yake kalla. Sai dai kuma ba kowa bane burinsa ke cika akan hakan duba da irin yadda fina-finan ke zuwa da nauyi sakamakon ingancin da yake tattare da hotuna da kuma sautin muryoyin dake cikinsu(misali unconverted Mp4s).
Wasu lokutan kuma kila ka bukaci tura ma wani hoton video da aka dauka wajen bukukuwa ko kuma wasu tarurruka ta hanyar facebook, whatsapp ko kuma ta wata kafar sadarwar amma nauyinshi sai ya hana ka yin hakan duba da yanayin network mara karfi, ko rashin chaji isashshe ko kuma yanayin iyakar nauyin da kafar da zaka tura ta ita ta kayyade(upload limit).
Mutane da yawa sun sha tambayata kan ko akwai wasu apps da zasu iya amfani dasu wajen rage wa video nauyi don samun space da kuma samun damar kara wasu vidiyoyin akan wayoyinsu. Bisa wadannan dalilan dana zayyano yasa na yanke shawarar binciko gami da yin rubutu akan yadda mutum zai iya ragewa video nauyi.....
A can baya akan iya ragewa video nauyi ne kawai ta hanyar amfani da kwamfyuta, amma yanzu cigaban zamani ya kawo da yadda za'a iya yin amfani da wayar hannu wajen cimma aikin...
Abubuwan da ake bukata:
Ba wasu abubuwa ne masu yawa muke bukata ba, illa dai kawai muna bukatar wayar da za'ayi amfani da, sannan kuma sai daya daga cikin wadannan manhajojin(apps):
(i) Audio/Video Converter Android (Download it from playstore or simply click Here)
(ii) Video compressor (samo shi daga store ko kuma ka shiga nan
Da Audio/Video Converter Android zaka iya rage nauyin video din da yaka kamar 500mb zuwa 180mb ba tare da ingancin(quality) sa ya baci ba.
Haka zalika ma video compressor zai iya rage nauyi video da yakai 500mb zuwa 180 ko 200mb ba tare da rasa inganci ba, sai dai kuma Audio/Video converter android yafi video compressor sauri...
Ina fatan yanzu ba zaku kara yin kukan karancin guri ba yayin da kuke son dora video me nauyi zuwa wayoyinku na hannu.
Ina fatan zaku tura wa abokanenku wannan rubutu nawa ta hanyar sharin zuwa facebook, whatsapp, twitter da sauransu don suma su amfana.. Yi amfani da share buttons dake kasa...

'Mun bai wa Majalisa mako biyu ta tabbatar da Magu'

Wasu 'yan Najeriya sun bai wa 'yan majalisar dattawan kasar wa'adin mako biyu da su tabbatar da Ibrahim Magu, a matsayin shugaban hukumar EFCC ko kuma su yi zanga-zanga a mazabun 'yan majalisar.
Sun bayyana hakan a wani taron manema labarai da suka gudanar a birnin Legas.
Sun kara da cewa duk wani yunkurin hana tabbatar da Ibrahim Magu a matsayin shugaban EFCC na dindindin zai iya yin zagon-kasa a yakin da Shugaba Muhammadu Buhari ke yi da cin hanci da rashawa.
A makon da ya gabata ne dai 'yan majalisar ta dattawan suka ki tabbatar da Magu a matsayin shugaban EFCC.
Sun ce sun yi hakan ne saboda rahoton sirri da suka samu a kansa na aikata ba daidai ba.
Sai dai shugaban na EFCC bai ce komai kan batun ba.
Shugaban masu rinjaye na majalisar Sanata Mohammed Ali Ndume ya shaida wa BBC cewa sun mika wa Shugaba Buhari rahoton, yana mai cewa suna jiran matakin da zai dauka kafin su yi yunkuri na gaba a kan Ibrahim Magu.
Wasu dai na zargin cewa takun-sakar da ake yi tsakanin hukumar tsaro ta DSS da EFCC ce ta sanya manyan jam'ian na DSS suke yi wa Ibrahim Magu bi-ta-da-kulli, kodayake ba su ce komai a kan zargin ba.

Dubban farar-hula na cikin mawuyacin hali a Aleppo

Dubban farar-hular da aka rutsa da su a Aleppo na kasar Syria na cikin mawuyacin hali a yayin da ake jan-kafa wajen aiwatar da yarjejeniyar da gwamnati da 'yan tawaye suka kulla ta kwashe su daga birnin.
Masu aiko da rahotanni sun bayyana cewa sun ga mutane na kwana a cikin matsanancin sanyi ba tare da samun abinci ba.
Da alama an samu jinkirin kwashe su ne saboda jayayyar da kan fitar da farar-hular daga yankuna biyu da ke hannun gwamnati a lardin Idlib.
Sai dai gidan talabijin gwamnatin Syria ya ce motocin bas-bas sun shiga gabashin Aleppo da rana domin soma kwashe farar-hular.
Rahotanni sun ce za a kwashe mutum 1,200 a bas-bas daga yankunan 'yan tawaye yayin da za a kwashe kamar wannan adadi daga garuruwa biyu da ke hannun gwamnati a lardin na Idlib.
Motocin bas-bas din sun shiga gabashin Aleppo ne karkashin kulawar kungiyar bayar da agaji ta the International Red Cross da takwararta ta the Syrian Arab Red Cross, in ji kamfanin dillancin labarai na Sana.

ƊDan ƙkunar-bakin-wake ya kashe sojoji da dama a Yemen

Wani dan kunar-bakin-wake ya kashe sojoji akalla 23 kana ya jikkata wasu da dama bayan ya tayar da bama-baman da ke jikinsa a birnin Aden mai tasoshin jiragen ruwa na kasar Yemen.
Rahotanni sun ce sojojin na kan layin karbar albashi kusa da barikinsu lokacin da dan kunar-bakin-wake ya tayar da bama-baman.
Mutumin ya saje da sojojin ne a barikin Al-Solban da ke gundumar Al-Arish, a cewar jami'an soji.
Hakan na faruwa ne bayan da a farkon makon da muke ciki wasu tagwayen hare-hare da aka kai wa sojoji suka yi sanadin mutuwar 48 daga cikinsu.
Babu wata kungiya da ta dauki alhakin kai harin na ranar Lahadi, sai dai masu ikirarin jihadi sun sha kai hare-hare a yankin.
A watan Agusta, wani harin kunar-bakin-wake da kungiyar IS ta yi ikirarin kai wa a wata cibiyar daukar sojoji aiki da ke birnin ya halaka akalla mutum 70.

Saturday, 17 December 2016

8 Best Twitter Tools To Unfollow Non Followers

Starting from the basics, we all are taught to connect and interact with people in social media platforms in order to boost engagement and build relationships. While this is a good practice, but in platforms like twitter, we often develop a mass of people we follow but they eventually don’t follow us.
Having a lot of people who don’t follow us is not a good sign as twitter only allows you to follow only 2000 accounts more than the number of users who follow you.
If you are tired of unfollowing those non-followers manually or removing fake and inactive twitter profiles from time to time, this post will demonstrate the top 8 twitter unfollow tools to mass unfollow non-followers.
twitter unfollow tools

Why should you unfollow on Twitter?

Unfollowing on twitter is most necessary when you are on it for a purpose. Here is why you are ethical when you unfollow twitter users:
  • Unfollowing the non-followers will actually give you the chance to connect with more twitter users. This is because you cannot follow more than 2000 people following you. It means if you don’t unfollow non-followers you are missing it out.
  • You are always welcome to unfollow people who blast out tweets. This will help you lessen the clutter off your newsfeed.
  • Unfollowing people not related or compatible with your business will make you have more time to concentrate with others who have enough opportunities for you.
Now let us see some of the tools that help you in the “unfollow clutter mission”
1

tweet adder twitter tool
Tweet adder is to twitter as jetpack is to WordPress. It has everything you would desire for marketing on twitter. I have personally used tweetadder and here is its reviewexclusive for the readers of bloggertipstricks.
Now coming to the unfollow features, tweet adder is a rocker. It has a wide range of filter unfollowing people. You can use tweetadder to:
  • Unfollow people who don’t follow you back or have recently unfollowed you.
  • Unfollow people with spam profiles like no profile picture or default egg gravatar.
  • Unfollow people who are too talkative or too quite (don’t tweet enough).
  • Unfollow people who speak a different language than you do.
2

social bro twitter tool
Socialbro is a very powerful twitter tool that is a must keep in your social media toolbox. Besides helping you to mass unfollow twitter users, Socialbro has a plethora of other functions like:
  • Audience insights: Gives you powerful insights about your follower stats.
  • Analyze competitor: It helps you to track the progress and efficiency of competitor twitter accounts by studying its changes in strategy, evolution with time etc.
  • Collaborators: It handles the teammates that work in your twitter strategy. You can control which team mate has how much access to your specific twitter account.
Coming to unfollow tool of socialbro it has a pretty simple yet powerful interface.
Just login to socialbrowith your twitter account. Go to the dashboard and click on the community option on the top bar. It displays all the users and many filters to show the unfollowers or people not following back.
3

unfollowers twiiter tool
Unfollowers.com or unfollowers.me is the most straightforward app to manage twitter followers. It has a clean layout and allows you to display users based on following.
In addition you can use it to send DMs, mention influencers and copy the followers list of influencers to grow your community.
The only demerit is it allows you to unfollow only 100 accounts per day in the free plan. This could be a pain if you are having a lot of inactive accounts. However once done it can be used to cut the follower list at regular intervals.
4

tweepi-twitter-tool
Want to make your twitter profile clean and engaged? Here is tweepi that has helped thousands of twitter users to follow as well as unfollow inactive people.
Formerly flush, the new twitter not following back option of tweepi is fast, precise and displays the exact synchronized list of most recent twitter accounts. You can easily use this to unfollow twitter users for free.
They have a premium plan too for more advanced features, but as far as unfollow tools are considered the free plan is more than enough.
5

crowdfire-twitter-tool
Crowdfire of Codigami Inc. had been formerly known as justunfollowers. This revamped name added more features to this free twitter management app but the unfollowers feature is as it was.
You can get rid of twitter accounts that are not following you and thus can keep your account clean. Crowdfire has dedicated android and IOS apps to help you clean your twitter profiles on the go.
The only drawback of this tool is it allows unfollowing only 25 followers daily which is quite low and could be time consuming when you want to use only the free version.
6

mangeflitter-twitter-unfollow-tool
This is a very reputed tool and has been featured in top social media blogs like buffer. ManageFlitter has also a unique feature that lets you unfollow the most talkative twitter accounts you follow. This will help you to keep your twitter account noise free and concentrate on important twitter news feed.
One of the coolest feature of manageflitter is it shows you the number of twitter user you have followed. That means if you see @moz it shows you the serial number at which you followed moz since the starting of your account. Not a necessity but cool!
It has many other visual pleasures and filters you would love once you log in.
7

friend or follow twitter unfollow tool
Friendorfollow is a plain and free way to unfollow users who are not following you back on twitter. It also similar features for tumblr and instagram users.
You can quickly see which friend is following you back and which not and thus unfriend them (or unfollow in terms of twitter).
You can also export this list of twitter users in a .csv file for future reference.
8

untweeps twitter unfollow tool
Untweeps is a great free twitter unfollow tool that lets you unfollow inactive twitter accounts. This is a wise step as a hundred active followers are far better than 1000 inactive users.
Just log in through your twitter account and enter a number to depict the number of days a twitter account is inactive since. This is helpful to categorize users who haven’t tweeted since a definite time and quickly unfollow them.
Over to you:
I think unfollowing the non-followers is wise and just because it will help our twitter profile not appear spammy. Moreover in order to appear authoritative you need to follow only accounts that provide value. So use these tweets to quickly unfollow your twitter followers that aren’t contributing much.
Do tell use which tools you use to unfollow twitter users.