Tuesday 27 August 2019

Kalli Iskancin Da Wata Budurwa Keyi Da Wani Tsoho Da Sunan Waka

Kai Jama’a duniya tazo karshe Wannan Wani Video Ne Da Muka Samu Yana Yawo A YouTube.

inda mukayi karo da wani tsoho tare da wata budurwa suna wata irin rawar iskanci da sunan Waka.

Wannan Video munyi karo dashi ne a wata tashar YouTube mai suna Arewafresh Tv channel.

Abin yayi muni sosai Ga videon Nan Dai Ku duba Kasa Ku kalla akan wayar ku Domin Ganin irin wannan Rashin Kunya.

Downlord mp4

Umar M Shareef – Fadli Falala New Song 2019

Sabuwar Wakar Umar, M Shareef Ta Wannan Shekarar 2019 Mai Taken Fadli.
wakar Tayi dadi sosai Daga bakin Shahararren Mawakinan Wato Umar M Sharif.

Downlord mp3

Saturday 18 May 2019

Kalli Zafaffan hotunan Jaruma Maryam Yola Nas

 Kyawawan Hotunan jaruma maryam yahya yola wanda tayi film din nas kuma tsohuwar matar Jaruma adam a zango.





Dalilin Da Ya Sa Nake Auri-saki – Adam Zango

Fitaccen jarumin nan na dandalin shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, Adam A Zango wanda aka fi sani da Prince Zango ya bayyana dalilin da ya sa yake yawan auran mata kuma daga bisani ya rabu da su. Jarumin ya bayyana cewa ba wai baya iya zama da mace bane, sai dai
" ba zan iya fada muku abin da ya hada shi da matata ta farko, da matata ta biyu da kuma matata ta uku ba."
“ Allah yana hada mata, mace da namiji. Allah ya halicci mata domin su kasance ni’ima a garemu maza. Don mu Allah ya halicce su."
Adam ya kuma bayyana cewa Allah ya rigada ya tsara ma mutum kaddararsa da abunda zai faru da shi tun kan a haifasa har izuwa ranar da zai amsa kiran mahallicinsa.
Dan wasan ya bayyana hakan ne a hira da yayi da shafin BBC Hausa inda yake cewa:
" Allah Ubangiji ya rubuta wa mutum abin da zai faru da shi tun daga farkon haihuwarsa har zuwa ranar mutuwarsa." “Kuma wannan kaddarar da Allah yayi mun itace tawa, saboda ni , Allah yana gani, Allah ya ba ni komai da na roke shi, amma ban da mace wanda nake zaman aure da su.
“Sannan kuma ina so na gayawa mutane wani abu cewa, duk mutin da ya kasance zai yi aure ya rabu da mace, ya kara yi kuma ya kara rabuwa da ita, toh ya kamata su gane cewa wannan mutumin ba mazinaci ba ne. Saboda ni Adamu Zango Allah ya ba ni, duk duniya a cikin masana’antar Kannywood, babu wanda mata ke so iri na. Toh me zan yi da aure?”

Ban Taba Tsammanin wani A Masana'antar kannywood Zai Iya kaini Kotu ba Balle Ali nuhu - Adam A Zango

Fitaccen jarumin fina-finan Hausan nan Adam Zango ya ce ya ji matukar kunya da mutumin da yake kira ubangidansa a masana'antarsu wato Ali Nuhu ya kai shi kara kotu.
Adamu ya ce bai taba tsammanin cewa wani a masana'antar zai iya kai shi kotu balle Ali.
"Ai muna da shugabanni, na yi tsammanin komai ya faru su za a gayawa su sasanta, amma sai aka kai kotu, gaskiya abin ya ban kunya," in ji Adamu.
A kwanakin baya ne dai jarumi Adam Zango ya wallafa wani sako inda ya yi ikirarin cewa tun da Ali ya sa aka zagi mahaifiyarsa shi ma sai ya rama.
Daga bisani ne Ali ya kai Adamu kotu, inda har aka aike wa Zangon sammaci.
Duk da yake a yanzu an sasanta jaruman biyu, sai dai ba dai wannan ne karo na farko da suka taba rikici har aka sasanta su ba, amma dai ba a taba batun zuwa kotu ba sai wannan karon.
Sai dai duk wannan rikici da ke faruwa tsakaninsu, a duk lokacin da BBC ta tuntubi Ali Nuhu ba ya cewa komai.
Ko a rigimar zuwa kotun ma, an tuntube shi kuma ya ce ba zai tofa komai ba sai dai a ji ranar zaman kotun.
A hirar tasa da Nasidi Adamu Yahaya kan batun kai masa sammacin, Adam ya kara da cewa: "Da na yi rubutu na zagi Ali ba alfahari nake da hakan ba, na san ba daidai ba ne.
"Sai dai daga bisani na fahimci abin da na yi ban kyauta ba, da nemansa na yi gaba da gaba na gaya masa maimakon shaida wa duniya.
"Amma na yi hakan ne saboda wadanda suka zage ni a dalilinsa su ma sun yada ne duniya ta gani."
Daga bisani dai an sasanta jaruman biyu da suka kasance na kut da kut a da.
"Amma daga baya manyanmu sun zaunar da mu sun sasanta mu, kuma na ba shi hakuri.
"Sai dai kamar yadda aka sa na ba shi hakurin nan, ai ya kamata shi ma a kalla ya sa yaransa masu zagina su ba ni hakuri ko da sau daya ne," in ji Zango.
HABAICI
A cikin hirar an kuma tabo Adamu kan dalilin da ya sa yake yawan yi wa makiyansa habaici a shafukan sada zumunta, sai ya ce yawan makiyan da yake da su ne ya sa yake yawan wallafa sakon habaice-habaice a shafinsa na Instagram.
Jarumin ya ce abin da ya dauka makiyi shi ne duk mutumin da ba ya bukatar ya ga "ci gabanka ko kuma idan ka yi wani abin burgewa, amma shi bai ga hakan ba, to makiyinka ne."
"Ko kuma mutumin da idan wani abu ya zo maka na karuwa kamar karramawa ko taron kalankuwa ko na biki, amma sai ya ce kar a bai wa wane, gara a bai wa wane, to makiyinka ne.
"Dole ne a masana'antarmu sai ka samu makiya, wasu na jikinka ne, ko daraktoci, ko jarumai ko furoduoshi ko 'yan wasa.
"Dan Adam bai son kishiya, duk wanda ya ga wani yana daga wa ko yana neman ya wuce shi a daukaka to zai ji haushi," a cewar Adamu.
Jarumin ya ci gaba da cewa idan ya yi maganar makiya to ba da mutum daya ko biyu yake ba, yana magana ne kan mutane da dama da suke nuna masa irin wadancan halayyar da ya ambata.
Wanda ya tsargu da shi ake.
Jarumin ya ce idan mutum ya yi habaici to duk wanda ya tsargu, tabbas yana cikin wadanda ya rubuta sakon saboda su.
"Sannan akwai masu bin mu wato fans, amma kuma makiya ne.
Za ka yi abin da ba wanda ya taba yi a duniya, amma sai su ce karya ne kwaikwayon wani ka yi.
"Don haka na kan yi wasu abubuwan ne don na burge masoyana, a hannu guda kuma na aikewa makiyana sako a fakaice cewa na san irin kiyayyar da suke min," in ji Adamu Zango.

BBChausa.

Friday 17 May 2019

Yadda Zaka Samu Kyautar 750MB A Kowanne Layi

Jama’a barkanku da wannan lokaci. A yau muna dauke da bayani akan yadda zaku more garabasar data ta browsing a kan kowanne layi( MTN, Airtel, Glo da kuma Etisalat).
Abubuwan da ake bukata
Wayar Android
Layin waya(ko wane irine)
Manhajar Flaim (zan baku link da zaku dauko ta a kasa).
Ba tare da bata lokaci ba, ka dauko wannan manhaja ta Flaim akan wayar android dinka (download link yana kasa)
Daga nan sai ka bude Manhajar za kaga gurin da aka bukaci mutum ya sanya lambar wayar shi, sai ka saka lambar taka.
Zasu turo maka verification message mai dauke da lambobi guda 6 wadanda zaka sanya a gurbin verification din.
Da zarar ka gama verification zaka ji anyo maka sakon data (750mb) ko kuma kati na kira (N500) a wayarka( sai ka duba yawan data dake kan layin zaka gani).
Daga nan zaka ga sun kai ka wajen da zaka sanya username da kuma status update naka, daga nan sai kuma kaga an kaika wajen sanya DP(Display Picture) ko kuma profile picture, shikenan ka gama sai dai in kana bukatar kari to zaka gayyato abokanenka ta hanyar “invite” button dake cikin manhajar.
ba zaka kulle wannan manhaja ta Flaim ba a yayin da kake jiran zuwan verification code din, sannan ka sani code din zai iya daukar kamar mintuna goma (10 minutes) kafin ya shigo, saboda haka sai mutum ya jira har sai sakon ya shigo.
Zaka sami karin data ko kudin kira a duk lokacin da ka gayyato abokanka sukayi register.
Domin sauke wannan manhaja ta Flaim sai.

Kotu Ta Bada Umarnin A Kamo Hadiza Gabon Cikin Awanni 24

RIKOCI TSAKANIN GABON DA NABRASKA

Kotu Ta Bada Umarnin A Kamo Hadiza Gabon Cikin Awanni 24
Wata Kotun Majistari da ke zama a Birnin Kano, karkashin jagorancin Alkali Muntari Gambo Dandago, ta umurci Kwamishinan ‘yan sandan Jihar Kano da ya kamo mata Jarumar Fim din Hausa, Hadiza Gabon. Sannan kuma kotun ta umurci kwamishinan ‘yan sandan da ya binciki zargin da mai kara, Jarumi Mustapha Naburaska ya shigar a kan zargin cin zarafinsa da Hadiza Gabon din ta yi.
Alkalin ya yanke wannan hukunci ne sakamakon kauracewa zaman kotu da Hadiza Gabon ta yi a yau Alhamis.
Idan dai ba a manta ba, tun a kwanakin baya ne Naburaska ya shigar da karar Gabon kan zargin cin zarafi.

Rariya