Saturday 31 December 2016

Home Ni ma zan iya amfani da karfi kan ECOWAS — Jammeh

Danna hoton don shiga whatsapp group dinmu πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡πŸ‘‡


Shugaban Gambia mai barin gado, Yahaya
Jammeh, ya ce, idan tura ta kai bango zai iya
yakar Kungiyar Habaka Tattalin arzikin Afirka ta
Yamma, ECOWAS ko kuma CEDEAO.
A wani sakon taya murnar sabuwar shekara ga
'yan kasar, da aka yada a kafar sada zumunta ta
Youtube, Jammeh, ya ce, kungiyar na wuce gona
da iri a Gambia.
Ya ce ECOWAS na nuna banbanci tsakaninsa da
Adama Barrow.
Saboda haka ne ya nemi kungiyar da ta san inda
dare ya yi mata domin a cewarsa bata da
hurumin yin katsalanda a kasar.
Yahya Jammeh dai ya ce shi ne mutumin da ya
lashe zaben kasar na farkon watan Disambar
2016, bayan da da fari ya amince da shan kaye.
Kungiyar ECOWAS dai a taron da ta yi a Abuja,
babban birnin Najeriya, ta ce, za ta iya amfani
da karfi wajen tunbuke Yahya Jammeh.

No comments:
Write Comments