Friday 17 May 2019

Home Kotu Ta Bada Umarnin A Kamo Hadiza Gabon Cikin Awanni 24

Danna hoton don shiga whatsapp group dinmu 👇👇👇👇


RIKOCI TSAKANIN GABON DA NABRASKA

Kotu Ta Bada Umarnin A Kamo Hadiza Gabon Cikin Awanni 24
Wata Kotun Majistari da ke zama a Birnin Kano, karkashin jagorancin Alkali Muntari Gambo Dandago, ta umurci Kwamishinan ‘yan sandan Jihar Kano da ya kamo mata Jarumar Fim din Hausa, Hadiza Gabon. Sannan kuma kotun ta umurci kwamishinan ‘yan sandan da ya binciki zargin da mai kara, Jarumi Mustapha Naburaska ya shigar a kan zargin cin zarafinsa da Hadiza Gabon din ta yi.
Alkalin ya yanke wannan hukunci ne sakamakon kauracewa zaman kotu da Hadiza Gabon ta yi a yau Alhamis.
Idan dai ba a manta ba, tun a kwanakin baya ne Naburaska ya shigar da karar Gabon kan zargin cin zarafi.

Rariya

No comments:
Write Comments