Sunday, 6 November 2016

Home Hare-haren IS sun halaka mutane 21 a Iraki

Danna hoton don shiga whatsapp group dinmu 👇👇👇👇


Kungiyar IS ta ce ita ce ta kai wasu hare-haren
kunar bakin wake biyu a biranen Tikrit da
Samarra na Iraki, inda ta kashe akalla mutane
21.
An kai dukkan hare-haren ne ta yin amfani da
motocin daukar marasa lafiya da aka shake su
da bama-bamai.
An tayar da daya daga cikin bama-baman ne a
kan layin motocin dake jira a bincike su a wurin
duba ababen hawa a Tikrit.
Shi kuma harin na Samarra, an kai shi ne a wurin
da ake ajiye motoci da masu ibada 'yan shi'a ke
amfani da shi.
Jami'ai sun ce 10 daga cikin wadanda suka
mutun 'yan kasar Iran ne.

No comments:
Write Comments