Wednesday, 2 November 2016

Wani Yarima ya sha bulala a Saudiyya
Rahotanni sun ce mahukunta a Saudiyya sun
zane wani Yariman gidan sarautar kasar bayan
da aka same shi da aikata laifi.
Wannan na zuwa ne makwanni kadan bayan da
aka kashe wani jinin sarautar kasar bisa laifin
kisan kai.
Amma kawo yanzu ba a bayyana suna ko ainahin
laifin da yariman ya aikata ba.
Sai dai ba kasafai ake samun jinin gidan sarautar
da laifi ba ko kuma a yanke musu irin wannan
hukunci.
Wasu masu amfani da shafukan sada zumunta a
kasar sun yi farin ciki da hukuncin, suna masu
cewa ya nuna yadda shari'ar Musulunci ke bi ta
kan kowa.
Kawo yanzu ba a bayyana wannan labari a
hukumance ba.
zane wani Yariman gidan sarautar kasar bayan
da aka same shi da aikata laifi.
Wannan na zuwa ne makwanni kadan bayan da
aka kashe wani jinin sarautar kasar bisa laifin
kisan kai.
Amma kawo yanzu ba a bayyana suna ko ainahin
laifin da yariman ya aikata ba.
Sai dai ba kasafai ake samun jinin gidan sarautar
da laifi ba ko kuma a yanke musu irin wannan
hukunci.
Wasu masu amfani da shafukan sada zumunta a
kasar sun yi farin ciki da hukuncin, suna masu
cewa ya nuna yadda shari'ar Musulunci ke bi ta
kan kowa.
Kawo yanzu ba a bayyana wannan labari a
hukumance ba.

El-Rufai ya sasanta rikicin masallacin Sultan Bello
Bangarorin da ke rikicin shugabanci a kan
masallacin Sultan Bello da ke Kaduna sun
sasanta bayan da gwamnatin jihar ta shiga
tsakani.
Matakin da gwamnan jihar ya dauka shi ne na
cewa a bar mataimakin limamin ya ci gaba da
limanci a matsayin wucin-gadi kafin a nada
limami na din-din.
Kwamitin masallacin bisa hadin guiwa da Sarkin
Zazzau, Alhaji Shehu Idris, da kungiyar Jama'atu
Nasril Islam da bangaren Dakta Ahmad Gumi da
sauran masu ruwa da tsaki su aka dora wa
alhakin nada sabon limamin.
A wata sanarwa da kakakin gwamnan jihar,
Samuel Aruwan, ya fitar, ya ce, an kawo karshen
rikicin ne bayan wani zama da bangarorin suka yi
a gidan gwamnati, wanda gwamnan jihar Nasir
Ahmad El-Rufai ya shirya.
Sanarwara ta ce bayan da gwamnan ya ji
bayanin dukkanin bangarorin da ke rikicin, ya ce
gwamnati ta shiga tsakani ne saboda tsaro
kawai, amma ba domin wani abu ba.
Sannan ya yi gargadin cewa gwamnati ba za ta
lamunta da duk wani mataki na karya doka ba da
sunan addini, da kuma barin mutane suna nema
wa kansu mafita ba kan wata matsala.
masallacin Sultan Bello da ke Kaduna sun
sasanta bayan da gwamnatin jihar ta shiga
tsakani.
Matakin da gwamnan jihar ya dauka shi ne na
cewa a bar mataimakin limamin ya ci gaba da
limanci a matsayin wucin-gadi kafin a nada
limami na din-din.
Kwamitin masallacin bisa hadin guiwa da Sarkin
Zazzau, Alhaji Shehu Idris, da kungiyar Jama'atu
Nasril Islam da bangaren Dakta Ahmad Gumi da
sauran masu ruwa da tsaki su aka dora wa
alhakin nada sabon limamin.
A wata sanarwa da kakakin gwamnan jihar,
Samuel Aruwan, ya fitar, ya ce, an kawo karshen
rikicin ne bayan wani zama da bangarorin suka yi
a gidan gwamnati, wanda gwamnan jihar Nasir
Ahmad El-Rufai ya shirya.
Sanarwara ta ce bayan da gwamnan ya ji
bayanin dukkanin bangarorin da ke rikicin, ya ce
gwamnati ta shiga tsakani ne saboda tsaro
kawai, amma ba domin wani abu ba.
Sannan ya yi gargadin cewa gwamnati ba za ta
lamunta da duk wani mataki na karya doka ba da
sunan addini, da kuma barin mutane suna nema
wa kansu mafita ba kan wata matsala.

'Yan Niger Delta sun mika bukatunsu ga gwamnati
Dattawan yankin Niger Delta a Nigeria sun
gabatar wa Shugaba Muhammadu Buhari
shawarwari 16 da suka ce za su taimaka wurin
samar da zaman lafiya a yankin.
A ranar Talata ne shugaban ya gana da wakilan
masu tayar da kayar baya da kuma shugabannin
al'umma da nufin kawo karshen hare-haren kan
bututan mai a yankin.
Shugaban ya shaida wa tawagar cewa matsalolin
da gwamnatinsa ta tarar a lokacin da ta karbi
mulki suna da yawan gaske, wadanda suka hada
da faduwar farashin mai, da kasa biyan albashi a
jihohi 27 daga cikin 36 na kasar.
Sauran matsalolin a cewar shugaban Najeriyar
sun hada da rashin tattalin dan abun da kasar ke
samu, lamarin da ya ce babu yadda za a yi a ci
gaba da tafiya a haka.
Hare-haren kungiyoyi irin su Niger Dealta
Avengers sun taimaka wajen kassara tattalin
arzikin kasar.
Jerin bukatun da tawagar ta gabatar sun hada da
gaggauta kammala manyan hanyoyin da aka fara
a yankin da kuma mayar da hedkwatar manyan
kamfanonin mai a Nigeriar zuwa yankin Niger
Delta, matakin da a cewarsu zai taimaka wajen
kara samar da ci gaba a yankin.
Shugabannin yankin Niger Deltan karkashin
jagorancin Chief Edwin Clerk sun kuma bukaci
gwamnatin tarayya da ta gaggauta share
dagwalon mai da ya mamaye wasu garuruwa a
yankin baya ga yankin Ogoni.
Haka kuma Shugabannin sun nemi gwamnati da
ta sake duba shirin afuwa ga tsagerun yankin
tare da tabbatar da cewa an samar da ayyukan
yi ga wadanda aka horas da su karkashin shirin
yin afuwa ko kuma a rika ba su dan abun hasafi.
Sun kuma sha alwashin ci gaba da tattaunawa
akai-akai a jihohi daban-daban na yankin a wani
mataki na ganin an samu dorewar zaman lafiya.
Sannan suka ce tuni aka fara ganin tasirin
tattaunawar da suke yi tsakaninsu wanda hakan
ya kai ga yanzu aka samu karuwar danyen mai
da ake hakowa zuwa sama da ganga miliyan
biyu.
Shugaba Buhari wanda ya ce yana jiran rahoton
wani kwamitin da ya dora wa alhakin sake nazari
a kan shirin yin afuwa ga tsegurun yankin Neja
Delta, inda daga nan ne gwamnatin sa za ta ga
bangaren da ta gaza domin yin gyara.
Tawagar karkashin kungiyar Pan Niger Delta
Forum ta kuma jaddada goyon bayanta ga
Shugaba Buhari bisa abin da ta ce kokarin
gwamnatinsa wajen tabbatar da hadin kan
al'ummar Nigeria a matsayin kasa daya.
gabatar wa Shugaba Muhammadu Buhari
shawarwari 16 da suka ce za su taimaka wurin
samar da zaman lafiya a yankin.
A ranar Talata ne shugaban ya gana da wakilan
masu tayar da kayar baya da kuma shugabannin
al'umma da nufin kawo karshen hare-haren kan
bututan mai a yankin.
Shugaban ya shaida wa tawagar cewa matsalolin
da gwamnatinsa ta tarar a lokacin da ta karbi
mulki suna da yawan gaske, wadanda suka hada
da faduwar farashin mai, da kasa biyan albashi a
jihohi 27 daga cikin 36 na kasar.
Sauran matsalolin a cewar shugaban Najeriyar
sun hada da rashin tattalin dan abun da kasar ke
samu, lamarin da ya ce babu yadda za a yi a ci
gaba da tafiya a haka.
Hare-haren kungiyoyi irin su Niger Dealta
Avengers sun taimaka wajen kassara tattalin
arzikin kasar.
Jerin bukatun da tawagar ta gabatar sun hada da
gaggauta kammala manyan hanyoyin da aka fara
a yankin da kuma mayar da hedkwatar manyan
kamfanonin mai a Nigeriar zuwa yankin Niger
Delta, matakin da a cewarsu zai taimaka wajen
kara samar da ci gaba a yankin.
Shugabannin yankin Niger Deltan karkashin
jagorancin Chief Edwin Clerk sun kuma bukaci
gwamnatin tarayya da ta gaggauta share
dagwalon mai da ya mamaye wasu garuruwa a
yankin baya ga yankin Ogoni.
Haka kuma Shugabannin sun nemi gwamnati da
ta sake duba shirin afuwa ga tsagerun yankin
tare da tabbatar da cewa an samar da ayyukan
yi ga wadanda aka horas da su karkashin shirin
yin afuwa ko kuma a rika ba su dan abun hasafi.
Sun kuma sha alwashin ci gaba da tattaunawa
akai-akai a jihohi daban-daban na yankin a wani
mataki na ganin an samu dorewar zaman lafiya.
Sannan suka ce tuni aka fara ganin tasirin
tattaunawar da suke yi tsakaninsu wanda hakan
ya kai ga yanzu aka samu karuwar danyen mai
da ake hakowa zuwa sama da ganga miliyan
biyu.
Shugaba Buhari wanda ya ce yana jiran rahoton
wani kwamitin da ya dora wa alhakin sake nazari
a kan shirin yin afuwa ga tsegurun yankin Neja
Delta, inda daga nan ne gwamnatin sa za ta ga
bangaren da ta gaza domin yin gyara.
Tawagar karkashin kungiyar Pan Niger Delta
Forum ta kuma jaddada goyon bayanta ga
Shugaba Buhari bisa abin da ta ce kokarin
gwamnatinsa wajen tabbatar da hadin kan
al'ummar Nigeria a matsayin kasa daya.

Mutane 18 sun mutu a rikici tsakanin Fulani da Manoma a Niger
A Jamhuriyar Niger, a kalla mutane 18 ne suka
mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a wani
kazamin fada daya barke tsakanin manoma da
makiyaya a jahar Tawa.
Jami'ai sun ce rikicin ya barke ne kusa da wani
kauye mai suna Bangui, da ke kudancin kasar.
Monoman dai na zargin Fulanin da barin
dabbobinsu shiga wasu gonaki tare da lalata
musu amfanin gona.
Rikici akan gonaki da sauransu tsakanin Fulani
makiyya da manoma ya zama tamkar ruwan dare
a kasashen yammacin Afirka, lamarin da kan kai
ga asarar rayuka.
mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a wani
kazamin fada daya barke tsakanin manoma da
makiyaya a jahar Tawa.
Jami'ai sun ce rikicin ya barke ne kusa da wani
kauye mai suna Bangui, da ke kudancin kasar.
Monoman dai na zargin Fulanin da barin
dabbobinsu shiga wasu gonaki tare da lalata
musu amfanin gona.
Rikici akan gonaki da sauransu tsakanin Fulani
makiyya da manoma ya zama tamkar ruwan dare
a kasashen yammacin Afirka, lamarin da kan kai
ga asarar rayuka.

'Yan Niger Delta sun mika bukatunsu ga gwamnati
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya gana
da shugabannin yankin Niger Delta, da nufin
kawo karshen hare-haren masu tada kayar baya
kan bututan mai a yankin.
Shugaba Muhammadu Buhari ya shaida wa
tawagar shugabannin yankin Neja - Delta, cewa
matsalar da gwamnatin sa ta tarar a lokacin da
ta karbi mulki suna da yawan gaske, wadanda
suka hada da faduwar farashin man, da rashin
iya biyan albashi da wasu jihohi 27 daga cikin
jihohi 36 na kasar.
Sauran Matsalolin a cewar shugaban Najeriyar
sun hada da rashin tattalin dan abun da kasar ke
samu, lamarin da ya ce ba bu yadda za'a yi a ci
gaba da tafiya a haka.
Shugaba Muhammadu Buhari wanda ya karbi
wasu jerin bukatu 16 da tawagar ta gabatar
masa, ya ce ya na jiran rahoton wani kwamitin
da ya dorawa alhaki sake nazari akan shirin yi
afuwa ga tsegurun yankin Neja Delta, inda daga
nan ne gwamnatin sa zata ga bangaren da ta
gaza domin yin gyara.
Jerin bukatun da tagawar ta gabatar sun hada da
gaggauta kammala manyan hanyoyin da aka fara
a yankin da kuma maida hedkwatar manyan
kamfanonin mai a Nigeriar zuwa yankin Niger
Delta, matakin da a cewar su zai taimaka wajen
kara samar da ci gaba a yankin.
Shugabannin yankin Niger Deltan karkashin
jagorancin Chief Edwin Clerk sun kuma bukaci
gwamnatin tarayya data gaggawa share
dagwalon mai daya mamaye wasu garuruwa a
yankin baya ga yankin Ogoni.
Haka kuma Shugabannin sun nemi gwamnati da
ta sake duba shirin afuwa ga tsagerun yankin
tare da tabbatar da cewa an samar da ayyukan
yi ga wadanda aka horas da su karkashin shirin
yin afuwa ko kuma a rika basu dan abun hasafi.
Sun kuma dau alwashin ci gaba da tattauna wa
akai-akai a jihohi daban-daban na yankin a wani
mataki da ganin an samu dorewar zaman lafiya.
Sannan suka ce tuni aka fara ganin tasirin
tattaunawar da suke yi tsakanin su wanda hakan
ya kai ga yanzu aka samu karuwar danyen mai
da ake hakowa zuwa ganga miliyan 2 da dubu
100.
Tawagar karkashin kungiyar Pan Niger Delta
Forum sun kuma jaddada goyon bayan su ga
Shugaba Buhari bisa abin da suka ce kokarin
gwamnatin sa wajen tabbatar da hadin kan
al'ummar Nigeria a matsayin kasa daya.
da shugabannin yankin Niger Delta, da nufin
kawo karshen hare-haren masu tada kayar baya
kan bututan mai a yankin.
Shugaba Muhammadu Buhari ya shaida wa
tawagar shugabannin yankin Neja - Delta, cewa
matsalar da gwamnatin sa ta tarar a lokacin da
ta karbi mulki suna da yawan gaske, wadanda
suka hada da faduwar farashin man, da rashin
iya biyan albashi da wasu jihohi 27 daga cikin
jihohi 36 na kasar.
Sauran Matsalolin a cewar shugaban Najeriyar
sun hada da rashin tattalin dan abun da kasar ke
samu, lamarin da ya ce ba bu yadda za'a yi a ci
gaba da tafiya a haka.
Shugaba Muhammadu Buhari wanda ya karbi
wasu jerin bukatu 16 da tawagar ta gabatar
masa, ya ce ya na jiran rahoton wani kwamitin
da ya dorawa alhaki sake nazari akan shirin yi
afuwa ga tsegurun yankin Neja Delta, inda daga
nan ne gwamnatin sa zata ga bangaren da ta
gaza domin yin gyara.
Jerin bukatun da tagawar ta gabatar sun hada da
gaggauta kammala manyan hanyoyin da aka fara
a yankin da kuma maida hedkwatar manyan
kamfanonin mai a Nigeriar zuwa yankin Niger
Delta, matakin da a cewar su zai taimaka wajen
kara samar da ci gaba a yankin.
Shugabannin yankin Niger Deltan karkashin
jagorancin Chief Edwin Clerk sun kuma bukaci
gwamnatin tarayya data gaggawa share
dagwalon mai daya mamaye wasu garuruwa a
yankin baya ga yankin Ogoni.
Haka kuma Shugabannin sun nemi gwamnati da
ta sake duba shirin afuwa ga tsagerun yankin
tare da tabbatar da cewa an samar da ayyukan
yi ga wadanda aka horas da su karkashin shirin
yin afuwa ko kuma a rika basu dan abun hasafi.
Sun kuma dau alwashin ci gaba da tattauna wa
akai-akai a jihohi daban-daban na yankin a wani
mataki da ganin an samu dorewar zaman lafiya.
Sannan suka ce tuni aka fara ganin tasirin
tattaunawar da suke yi tsakanin su wanda hakan
ya kai ga yanzu aka samu karuwar danyen mai
da ake hakowa zuwa ganga miliyan 2 da dubu
100.
Tawagar karkashin kungiyar Pan Niger Delta
Forum sun kuma jaddada goyon bayan su ga
Shugaba Buhari bisa abin da suka ce kokarin
gwamnatin sa wajen tabbatar da hadin kan
al'ummar Nigeria a matsayin kasa daya.
Tuesday, 1 November 2016

Manchester City ta ci Barcelona 3-1
Manchester City ta doke Barcelona da ci 3-1 a
gasar cin kofin zakarun Turai da suka kara a
ranar Talata a Ettihad.
Barcelona ce ta fara cin kwallo ta hannun Lionel
Messi minti na 21 da fara wasa.
Sauran minti shida a je hutu ne City ta farke ta
hannun Ilkay Gundogan, Kevin de Bruyne ya ci ta
biyu bayan da aka dawo daga hutu, sannan Ilkay
Gundogan ya ci ta uku kuma ta biyu da ya ci a
karawar.
Da wannan sakamakon, Barcelona ta ci gaba da
zama a mataki na daya a kan teburin rukuni na
uku da maki tara, yayin da City ke matsayi na
biyu da maki bakwai.
Borussia Monchengladbach wadda ta tashi
kunnen doki 1-1 da Celtic a wasa na biyu na
cikin rukuni, tana mataki na uku da maki hudu
sai Celtic mai maki biyu.
Ga sakamakon sauran wasannin da aka buga:
Besiktas 1 vs Napoli 1
Basel 1 vs Paris St G 2
Ludogorez 2 vs Arsenal 3
Benfica 1 Dynamo Kiev 0
Atl Madrid 2 vs FC Rostov 1
PSV Eindhoven 1 vs Bayern Munich 2
gasar cin kofin zakarun Turai da suka kara a
ranar Talata a Ettihad.
Barcelona ce ta fara cin kwallo ta hannun Lionel
Messi minti na 21 da fara wasa.
Sauran minti shida a je hutu ne City ta farke ta
hannun Ilkay Gundogan, Kevin de Bruyne ya ci ta
biyu bayan da aka dawo daga hutu, sannan Ilkay
Gundogan ya ci ta uku kuma ta biyu da ya ci a
karawar.
Da wannan sakamakon, Barcelona ta ci gaba da
zama a mataki na daya a kan teburin rukuni na
uku da maki tara, yayin da City ke matsayi na
biyu da maki bakwai.
Borussia Monchengladbach wadda ta tashi
kunnen doki 1-1 da Celtic a wasa na biyu na
cikin rukuni, tana mataki na uku da maki hudu
sai Celtic mai maki biyu.
Ga sakamakon sauran wasannin da aka buga:
Besiktas 1 vs Napoli 1
Basel 1 vs Paris St G 2
Ludogorez 2 vs Arsenal 3
Benfica 1 Dynamo Kiev 0
Atl Madrid 2 vs FC Rostov 1
PSV Eindhoven 1 vs Bayern Munich 2

Koriya ta Kudu: Park na binciken aminiyarta
Shugabar kasar Koriya ta Kudu Park Geun-Hye,
ta sauya Firaiminista da Ministan kudin
gwamnatin ta, a kokarin kaucewa danbarwar
siyasa da ta hada da wata aminiyarta.
Ana zargin kawar ta mai suna Choi Soon-sil, da
kokarin amfani da ita dan cimma manufar samun
kudade, kuma tuni aka tsare ta saboda gudun kar
ta yi kokarin tserewa daga kasar.
Wakilin BBC yace shugaba Parka na cikin tsaka
mai wuya saboda masu shigar da kara sun
gurfanar da kawar ta da suka shafe shekaru 40
tare gaban kuliya, ana tuhumar ta da ko ta na
amfani da kawancen da ke tsakanin ta da
shugabar kasar ta hanyar samun kudade daga
kamfanonin.
Wakilin ya kara da cewa ba a bayyana ko
ministocin an sallame su daga bakin aiki ba, ko
kuma su ne suka zabi barin aiki, ko kuma an
same su da hannu a badakalar da ta taso ba.
ta sauya Firaiminista da Ministan kudin
gwamnatin ta, a kokarin kaucewa danbarwar
siyasa da ta hada da wata aminiyarta.
Ana zargin kawar ta mai suna Choi Soon-sil, da
kokarin amfani da ita dan cimma manufar samun
kudade, kuma tuni aka tsare ta saboda gudun kar
ta yi kokarin tserewa daga kasar.
Wakilin BBC yace shugaba Parka na cikin tsaka
mai wuya saboda masu shigar da kara sun
gurfanar da kawar ta da suka shafe shekaru 40
tare gaban kuliya, ana tuhumar ta da ko ta na
amfani da kawancen da ke tsakanin ta da
shugabar kasar ta hanyar samun kudade daga
kamfanonin.
Wakilin ya kara da cewa ba a bayyana ko
ministocin an sallame su daga bakin aiki ba, ko
kuma su ne suka zabi barin aiki, ko kuma an
same su da hannu a badakalar da ta taso ba.
Subscribe to:
Posts (Atom)

