Saturday, 29 October 2016

Kyawawan halayen Hadiza Gabon

Hadiza ko kuma Dijatou Aliyu wadda aka fi
sani da Hadiza Gabon, tana daya daga cikin
jarumai mata da suka shahara a farfajiyar
finafinan Hausa. Hadiza ta yi matukar
kwarewa a duk wani matsayin da za a ba ta
a fim, wanda hakan ya sa har yau ake
damawa da ita a masana’antar, domin ba
kowace jaruma ba ce za ta iya hawa irin
matsayin da jarumar ke hawa a finafinai.
Fitacciyyar Jarumar Kannyywood, Hadiza
Gabon
Kyakkyawar jarumar ta kuma kasance mai
yawan masoya daga cikin jaruman fim, har
ta kai ga ta samu daukakar da ita kanta ba
ta taba zaton samu ba.
Allah ya azurta jarumar da kyawawan dabi’u
na taimako, tausayi da jin kan mutane,
musamman gajiyayyu, marasa karfi da kuma
marayu.
Akwai lokacin da labarin wata nakasashiyar
yarinya mai suna Rahama Karuna wacce ake
dauka a cikin roba ana bara da ita a jihar
Kano, lokacin da Hadiza ta ji labarin wannan
yarinya sai ta tausaya sosai harma ta ziyarci
yarinyar inda ta tallafa mata da kudade da
kayayyakin abinci.
Sannan kwanakin baya Hadiza ta ziyarci
sansanin yan gudun hijira inda su ma tayi
masu alkhairi mara misali, domin ta tallafa
masu da kayan abinci, kamar yadda muka
sani cewa yan gudun hijira sunyi fama da
lalurar yunwa.
Hadiza Gabon a lokacin da ta kai ziyara
sansanin yan gudun hijira
Bayan nan kuma a lokacin da jaruma Hadiza
za ta yi bikin zagayowar ranar haihuwarta,
maimakon ta tara jama’ar da ba su dace ba
a yi ta sharholiya, sai ta tattara kayayyakin
bikin nata ta je gidan marayu, inda ta dauke
su a matsayin wadanda za su taya ta bikin.
Hadiza ta yanka kek din bikin ranar
haihuwarta ta tare da marayun kuma ta ci ta
sha tare da marayun, domin a cewarta yin
hakan wata hanya ce ta farantawa marayun
rai, tare kuma da debe musu kewa, wanda
bai kamata a ce ana mayar da su saniyar
ware ba a al’amuran farin ciki dake gudana a
kasar nan.

Hadiza Gabon tare da wasu yara
Wannan ba shi ne karo na farko da Hadiza ta
kai ziyara gidan marayu ba, domin aikinta ne
ziyara gidan marayun inda take raba musu
kayan abinci da kayan sawa.
Munayi wa wannan jaruma fatan alkhairi da
kuma ci gaba a rayuwarta ta duniya da
lahira.

Darajar farashin Naira ta tashi

Darajar farashin Naira ta daga a
Bankunan Najeriya
– Naira ta daga da kusan Kobo 50 a Bankin
canji na Kasar
– A yanzu haka, Dalar Amurka tana kan
N305
Darajar farashin Naira ta samu yunkurawa
sama a Bankin canjin kudi na Najeriya. Kudin
Naira na Najeriya ya samu dagawa da abin
da ya kusa kai N1 a banki, sai dai kuma
Naira ya sauka a kasuwar canji, Inji Hukumar
Dillacin labarai na Kasa watau NAN
Darajar farashin Naira ta samu dagawa daga
N304.5 zuwa N305 a kan kowace Dalar
Amurka guda, ma’ana dai Naira ta kara
daraja da Kobo 50 watau Rabin kwandala.
A kasuwar canji kuma, watau Bureau De
Change, ana canjin dalar Amurka ne da Naira
N385, yayin da kuma ake sayar da kudin
Pound Sterling na Ingila a kan N560, ana
kuma canjin Kudin EURO na Turai a kan
N503 kan kowane guda.
Ma’ana dai Naira ta kuma fadi a kasuwar
‘Yan canji da ake kira Bureau De Change da
har kusan N5 duk da cewa farashin Naira ya
daga a Bankunan Kasar. Shugaban ’Yan
Canjin na Kasa, Malam Aminu Gwadabe yace
kwanan nan Darajar farashin Naira zai daga
sama, domin kuwa Bankin Kasar na shirin
yin wani abu a kan matsalar da ake
fuskanta.

Hotunan Rahama Sadau Tare Da Akon A Los Angeles


Rahama sadau ta amsa gayyatar da wasu jaruman Hollywood; akon da Jeta amata sukayi mata don su yi wani wasan kwaikwayo mai taken "The American King" wanda zasu shirya shi a wasu birane na kasar Amurka , Senegal South Africa da Nigeria.
Idan baku mance ba a kwanakin baya ne kungiyar masu tace fina-finai MOPPAN ta kori Rahama sadau daga kannywood bayan wani hoton video na waka tare da classiq inda ta nuna wasu dabi'u da basu dace da kundin tsarin kannywood ba.
A yanzu haka dai rahama sadau din tana birnin Los angeles don gudanar da wannan film din wanda za'a dauka a watan December mai zuwa.

Na fi so Ronaldo ya lashe Ballon d'Or — Zidane



Kocin Real Madrid Zinedine Zidane ya ce
Cristiano Ronaldo ne ya fi cancanta ya zama
zakaran kwallom kafar duniya duk da cewa bai
zura kwallaye da yawa a bana ba.
Zidane ya kara da cewa Ronaldo yana gaban
Lionel Messi wajen dacewa da lashe gasar ta
Ballon d'Or.
Ronaldo, mai shekara 31, na cikin 'yan wasan da
aka sanya sunayensu domin fafatawa wajen
lashe gasar bayan ya jagoranci Portugal ta dauki
kofin Euro 2016.
Sai dai ya yi ta samun koma-baya a kakar wasa
ta bana, inda ya zura kwallaye hudu kacal a
wasanni tara da ya buga.
Kocin na Real Madrid, Zidane, ya ce Ronaldo ne
"mutumin da ya fi dacewa da lashe gasar ba wai
don rawar da ya taka shi kadai ba, sai domin
tallafa takwarorinsa da yake yi domin su zura
kwallo."
Zidane ya ce Ronaldo ya san cewa nasarar da
yake tamu ta faru ne sakamakon aiki tukuru da
yake yi da kuma taimakwa 'yan wasan da ke tare
da shi.
Ronaldo, wanda sau uku yana lashe Ballon d'Or,
da kuma mai rike da kambun gasar Messi na
cikin 'yan wasa 30 da aka ware sunayensu domin
lashe gasar ta bana.
Dan wasan ya zura kwallaye 368 a fafatawa 357
da ya yi tun lokacin da ya koma Real Madrid
daga Manchester United a shekarar 2009.

Kompany zai ci gaba da murza leda a City -Guardiola

Kocin Manchester City Pep Guardiola ya ce
Vincent Kompany na da kyakkyawar makoma a
kungiyar, amma yana bukatar sadaukawar domin
ya rika buga wasa akai-akai bayan raunin da ya
ji.
Kompany, wanda ya buga wa City wasa sau 22 a
kakar wasan da ta wuce, ya ce ya gaji a lokacin
wasan da suka yi da Manchester United ranar
Laraba, lamarin da ya sa aka maye gurbinsa da
Aleksandar Kolarov.
Guardiola ya ce, kwantaraginsa ba ta tare a
kungiyar ba don haka babu inda za shi, yana mai
cewa "Ya ji rauni sau da dama. Amma muna
kokarin sake ba shi damar buga wa."
Kompany ya dauki kofin Premier sau biyu a City
a shekarar 2012 da 2014, amma raunukan da ya
rika ji sun hana shi katabus a bana.
Ya buga wa City wasa 33 a shekarar 2014 zuwa
2015, kasa da wasa 37 gabanin hakan.
Kompany ya koma City ne daga Hamburg a
watan Agustan shekarar 2008 kuma
kwantaraginsa zai kare a shekarar 2019.

Ba za mu kori Rooney ba —Mourinho

Kocin Manchester United Jose Mourinho ya ce
babu inda kyaftin din kungiyar Wayne Rooney
zai je.
Mourinho ya yi watsi da rahotannin da ke cewa
an gaya wa dan wasan ya fice daga Old Trafford
zuwa wata kungiyar idan yana so a rika sanya
shi a wasa.
Rooney, mai shekara 31, bai buga wasannin lig
ba tun bayan fafatawar da ta yi da Watford inda
suka tashi da ci 3-1 ranar 18 ga watan Satumba,
kuma bai shiga wasannin biyu na karshe da
kungiyar ta yi ba saboda ya ji rauni.
Mourinho ya shaida wa 'yan jarida cewa,"Babu
wata matsala da dan wasan ke fuskanta, amma
na san kun rubuta labaranku ne domin ku sayar
da jaridunku."
A cewarsa,"Rooney babban dan wasa ne wanda
ke da matukar muhimmanci a gare mu. Babu
inda za shi- muna kaunarsa. Ba ya jin dadi ne
kawai saboda an bar shi a benchi sannan kuma
ya ji rauni."
Yanzu dai Rooney ya murmure daga raunin da ya
ji.
Kwallaye hudu ne kawai suka rage masa,
wadanda idan ya zura su zai wuce Sir Bobby
Charlton wanda ya zura wa United kwallaye 249,
ya zama gagara-badau.
But he has scored just once this season and has
not found the net in his last 10 games for
United.
Mourinho ya kara da cewa 'yan jarida sun yi
masa kazafi da suka ce zaman da yake yi shi
kadai a Manchester tamkar wani "bala'i" ne ya
same shi.

Ana rikici kan limancin Masallacin Sultan Bello

Rundunar 'yansanda a jihar kaduna ta Najeriya ta
ce ta kama mutane 14 a yayin wata hatsaniya da
aka yi kan limacin masallaci mafi girma a jihar-
wato masallacin Sultan Bello.
Rikicin ya barke ne yayin sallar Jumu'a tsakanin
magoya bayan Sheikh Ahmad Mahmud Gumi da
na Dokta Khalid Aliyu wanda aka nada a
matsayin limamin masallacin na bayan tube
limamin na baya.
Magoya bayan Sheikh Ahmad Gumi na adawa da
nadin Dokta Khalid ne a zaman limamin
masallacin inda suke ganin gwanin nasu ne ya
kamata a nada.
Duka manyan malaman biyu dai sun dora alhakin
tashin hankalin kan junansu.
A wani taron manema labarai daya daga cikin
kungiyoyin musulmi mafi girma a kasar -
Jama'atul Nasril Islam ta yi Allah-wadai da
wannan lamari,inda ta yi kira ga gwamnati ta sa
baki kafin alamurra su kazance.